Magama MAGAMA Yuni/Juli 2019 | Page 4

RAHOTON ZAVE Mahangar mai sa’ido a harkar zave Daga Temitayo Famutimi R ichard hamshaqin mai hada-hadar kaddarorin gidaje da filaye ne da ke zaune a Legas. Ya yi tafiya zuwa qauyensu da ke Qaramar Hukumnar Aniocha ta Arewa da ke Jihar Dalta kafin zaven Shugaban qasa da aka tsara gudanarwa a ranar 16 ga Fabrairu. Cikin zaquwar farin ciki, har ta kai ga ya kasa yin barci a daren 15 ga Fabrairu. Ya farka da safe sai ya ji labari mai tayar da hankali; kimanin sa’ao’I biyar ya rage a fara gudanar da zave sai Hukumar Zave ta qasa (INEC) da ke da alhakin gudanar da zaven ta bayar da sanarwar xage zave zuwa mako guda. Richard ya ji takaicin jin cewa an xage zaven. Duk da haka sai ya qara wa’adin zamansa a qauye zuwa makonni uku don tabbatar da cewa an yi zavukan da shi, wato wanda aka xage na shugaban qasa da na gwamna da ke qaratowa. “Ban tava fashin yin zave ba tun bayan da Najeriya ta dawo mulkin farar hula cikin shekarar 1999. A gaskiya, saboda haka wannan shekarar ma ba zan qi yi ba,” kamar yadda ya bayyana mini. Richard na xaya daga ximbin ’yan Najeriya masu kishin qasa waxanda suka yi takakka zuwa xaukacin faxin qasar don a yi zave tare da su. A gaskiya, akwai rahotannin da ke nuna cewa ’yan Najeriya daga nahiyar Arewacin Amurka da Turai da Asiya sun dawo qasar don shiga a yi zavuka tare da su. Cike da zaquwa tare da son a aji su, Richard da sauran mutanen karkarar sun halarci rumfunan zave tun wajen qarfe 6:30 na safe. Sai dai kayan zave da jami’ai duk ba su zo wajen ba har zuwa qarfe 8:15 na safe. An dai fara yin zaven wajen qarfe 9:10 na safe. A xaukacin faxin qasar ’yan qasa sun jajirce wajen ganin sun yi amfani da damar ’yancinsu na kaxa quri’unsu. 4 MAGAMA | Mayu/Yuni 2019 A Asaba babban birnin Jihar Dalta, ba a fara yin zave ba a wurare da dama har zuwa qarfe 11 na safe. Can kuwa a Firamaren Uzoigwe, wata Cibiyar yin rajista mai xauke da rumfunan zave kimanin 12, xaruruwan masu kaxa quri’in sun yi takaicin makararar da aka yi na fara zaven. Ximbin na’urorin tantance katunan zave (Card Readers) ba sa aiki. Da yawan masu zave sun harzuqa, xaukacin matasa da tsofaffi, an gan su suna ta neman masu aikin sa’ido na cikin gida da waxanda suka zo daga qasashen duniya, don su nuna musu rashin jin daxin su (kan lamarin da ya faru). Wani mutum ya yi ihu da furta cewa “Babu wanda zai bar wurin nan har sai dukkanmu mun kaxa quri’unmu.” zaman lafiya. Kwanaki biyu kafin zaven gwamnoni, sarakunan gargajiyar Sagamu sun yi al’adun addinin gargajiya iri-iri don tabbatar da nasarar wajen tsoratar da miyagun mutane da masu yunqurin satar akwati da masu tayar da rikici. Duk da makarar da aka yi wajen fara zaven, al’amarin da ya kawo cikas na kashin farkon zavukan 2019, ’yan Najeriya sun nuna muhimmancin zaven gwamnoni da ’yan majalisar jihohi, inda aka samu qaruwar waxanda suka fito don kaxa quri’unsu in an kwatanta da waxanda suka fito zaven shugaban qasa. Ana ganin gwamnatocin jihohi a matsayin gwamnatin da ke yin tsare-tsare masu tasiri a rayuwar yau da kullum ga mafi yawan ’yan qasa. Duk da haka an samu ximbin matsaloli da suka haifar da cikas ga nakasassu da tsofaffi tukuf-tukuf, domin rukunin irin waxannan mutanen sun kasa isa waxannan rumfunan zave. Babu quri’un zaven da aka tanada don makafi, ko tabaron kambama hotuna ga mutumin da idanunsa ba su da qarfin gani a ximbin rumfunan zave da ke jihohin Ogun da Dalta. A xaya daga rumfunan zaven da ke Qaramar Hukumar Sagamu ta Jihar Ogun, masu kaxa quri’u sun qanqame kujerun wata makarantar elemantare da ke kusa da wurin, inda suka jeru kan layi a zaune. Duk suna riqe da lema don kare kansu daga zafin rana. Wurin zaven dai ya nuna a natse ake, amma dai akwai jami’an tsaro. Da yake an fafata zaven gwamna mai zafi a jihar, sarakunan gargajiya sun yi matuqar taimakawa wajen tabbatar wa al’umma da muhimmancin zaman lafiya. Tawagarmu ta fahimci cewa muhimman sarakunan gargajiya sun yi taro a xakin taro, tare da talakawansu inda suka buqace su da su bai wa Hukumar zave ta INEC haxin kai da ’yan sanda don tabbatar da A rumfar zaven da ke Qaramar Hukumar Ikenne a Jihar Ogun, wani mataimakin jami’in gudanar da zave an hango shi yana taimaka wa wani tsoho mai shekara tamanin bayan da ya kammala kaxa quri’arsa a matsayinsa na xan qasa. An hango mata masu juna biyu da masu nakasa da aka ba su fifikon muhimmanci wajen ba su damar kaxa quri’a a rumfunan zave da dama da ke faxin yankin. Daidai lokacin da aka kammala zaven 2019, akwai buqatar a yi kyakkyawan nazari kan yadda aka gudanar da zavukan. Tashe- tashen hankula da aka samu ba ta kamata a yardar da aukuwarsu a qasar da ake da wayewar kai ba, sannan a yi tur da su a matsayin abin qi. Ta fuskar sufuri da horar da ma’aikatan zave da dogaro da takardun quri’un da ake jefa wa akwati da tsarin tsaro – xaukacin waxannan al’amura xaya bayan xaya sai an yi musu cikakken nazari. Sannan zai yi matuqar fa’ida ga Hukumar zave ta qsaa INEC ta bibiyi irin shawarwarin da masu aikin sa’ido a zave na cikin gida da ’yan qasashen waje suka bayar don inganta tsarin gudanar da zavuka nan gaba. Najeriya bai kamata ta bari a ci gaba da maimaita mtsalolin da aka fuskanta a zaven 2019 ba, don ka da su sake aukuwa.