Magama Disamba 2018/Janairu 2019 | Page 3

SAQON JAKADA W. Stuart Symington Jakadan Amurka a Najeriya Saqon Jakada Maraba da wannan fitowar ta Magama A daidai lokacin da mutanen Najeriya ke tunkarar babban zave a shekara mai zuwa, xaukacinmu da ke Ofishin Jakadancin Amurka muna hanqoron ganin mun shaida yadda za a gudanar da zaven hart a kai ga ya samu nasarar da ta zarta wada aka samu a zavukan shekarar 2015, waxanda aka tabbatar da gudanarsu cikin lumana tare da MAGAMA Ana wallafa ta ne a bayan kowane wata uku a sashen Hulxa da Jama’a na Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya TAWAGAR EDITOCI Aruna Amirthanayagam (Shugaba kan Harkokin Hulxa da Jama’a) Russell Brooks (Jami’in Hulxa da Jama’a a Legas) Glenn Guimond (Jami’in Aikin Jarida) Olaoluwa Aworinde (Edita da Daukar Hoto) Xaukacin sakonni a aike ta wannan adireshi: Ga Editan, Mujallar Magama Sashen Hulxa da Jama’a na Ofishin Jakadancin Amurka Plot 1075 Diplomatic Drive, Central Business Area, Abuja, Nigeria Tel: (09) 461-4000. Fax: 09-461-4305 OFISHIN LAGOS: Ofishin Jakadancin Amurka 2, Walter Carrington Crescent, Lagos Tel.: +234-703-150-4867/2444 E-mail: [email protected] Website: ng.usembassy.gov inganci da sahihanci. A wannan fitowar, mun bayyana wasu daga ayyukanmu na haxin gwiwa da ’yan Najeriya don cimma managarciyar manufa. Mun gana da jiga-jigan gwamnatin Najeriya da manyan masu ruwa da tsaki a harkar zave da shugabannin siyasa da qungiyoyin fafutikrar haqqoqin al’umma, tare da xaukacin al’umma waxanda za su kaxa quri’a a wajen zave. Xan takararmu kawai shi ne tsarin gudanarwa. Manufarmu ita ce taku; a tsarin da zai kasance yin gaskiya qeqe-da-qeqe da nagarta da tsafta da adalci da za su wanzar da zaman lafiya. Zavukan da za su tabbatar da cikar burin mutanen Najeriya. Ziyarar kwanan nan da Mataimakin Sakataren Harkokin Afirka na qasar Amurka, Tibor Nagy ya kawo Najeriya, ta fito da irin wannan manufa tamu. A ziyararsa ta kwanaki biyu, ya gana da Shugaban Hukumar Zave ta Qasa, da Sarkin Musulmi, Sultan na Sakkwato tare da wasu jiga-jigan shugabannin jam’iyyun siyasa. Muhimmin saqon da ya isar ga kowa-da-kowa a cikin waxanda ya gana da su, shi ne, kamar yadda na bayyana tun farko, Amurka na mara wa xan takara guda baya ne a waxannan zavuka, kuma shi (xan takarar) ba wani ba ne, illa tsarin gudanar da zavuka. Babu wani burin a qaqava wani mutum, ko fifita buqatun wata jam’iyyar siyasa a kan haqqoqin mutanen Najeriya da ke da ’yanci/ haqqin zaven wanda suke so ya jagorance/ shugabancesu. Akwai ximbin masu ruwa da tsaki a zave. Mafi muhimmanci su ne masu kaxa quri’a. Kowane mutum da ya cancanci kaxa quri’a, ya yi rajista da hukumar zave ta qasa (INEC), kuma ya mallaki kazin zavensa/ta na dindindin, don haka haqqi ne da ya rataya a kansa/ta wajen tabbatar da an gudanar da zave cikin lumana don tabbatar da cewa sun kaxa quri’unsu an tattara an qirga. Da zarar ka/kin aikata hakan tare da kowane xan/’yar qasa a cikin al’ummarka/ki a xaukacin faxin qasar nan, babu mugun/azzalumin da zai hargitsa tsarin ya vata maka/ki makoma. Sauke wannan xauyi zai sanya ka/ki zama mai kare kyakkyawar makomar Najeriya, tare da tabbatar da ’yanci da yalwar walwala a faxin duniya da za ta amfanar da xaukacinmu gaba xaya. A sha karatu lafiya. Jakada W. Stuart Symington A wannan fitowar Babban Labari Tarairayar mutanen Najeriya Shafi na 4 Shafi na 10 Qarancin Shekaru ba ya hana Takara Zaven Osun Shafi na 7 Shafi na 13 Babban Taron YALI Makoko Shafi na 8 Shafi na 14 Dabarun Sabunta Qarin Shiri A biyo mu: Shafi na 9 Bugu na 22 Lamba na 3 Gasar Hotunan NaijaGEMs a Legas Shafi na 18 MAGAMA | Disamba 2018/Janairu 2019 3